logo

HAUSA

Faransa ta sanar da rufe ofishin jakadancinta da ke Nijar

2023-12-25 10:19:42 CGTN HAUSA

 

Dangantaka tsakanin Nijar da Faransa ta kai karshen bango, bayan da a wannan mako a cikin wata sanarwa ta ranar 19 ga watan Disamba wacce ta tabbatar da rufe ofishin jakadancin Faransa da ke birnin Yamai na jamhuriyar Nijar. Matakin da ya turo ’yan Nijar da dama masu bada hidima a ofishin jakadancin rasa aikinsu.

Daga birnin na Yamai, abokin aikinmu Mamane Ada ya duba wannan batu ga kuma rahoton da ya aiko mana.