logo

HAUSA

Kamfanin gine-gine na kasar Sin CGC zai gina gadojin kasa biyu a jihar Kano

2023-12-23 15:04:06 CMG HAUSA

 

Gwamnatin jihar Kano dake arewacin Najeriya ta bayar da kwangilar naira biliyan 15.97 ga kamfanin China Geo-engineering Corporation CGC domin gudanar da aikin ginin gadojin kasa a cikin birnin Kano.

Kwamashinan yada labarai na jihar Baba Halilu Dantiye ne ya tabbatar da hakan jiya Juma’a 22 ga wata lokacin da yake ganawa da manema labarai a ofishinsa. Ya ce, aikin ginin gadojin za a gudanar da su ne a shatale-talen unguwar Dan-Agundi da kuma na Tal’udu.

Daga tarayyar Najeriya wakilin mu Garba Abdullahi Bagwai ya aiko mana da rahoto.