logo

HAUSA

Hadin gwiwar Sin da Ghana na da muhimmanci ga ci gaban tattalin arzikin Ghana

2023-09-28 11:13:58 CMG Hausa

Ministan kudi na kasar Ghana Kenneth Ofori-Atta, ya ce hadin gwiwar Sin da kasarsa, ya kasance mai matukar muhimmanci ga ci gaban tattalin arzikin kasar ta yammacin Afrika.

Cikin jawabin da ya gabatar da yammacin ranar Talata a wani biki da aka yi albarkacin cika shekaru 74 da kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin, Ofori-Atta ya yabawa kasar Sin bisa dimbin goyon bayanta ga kasar Ghana a dukkan fannonin tattalin arziki, ciki har da taimakawa kasar samun rancen dala biliyan 3 daga asusun bada lamuni na duniya.

Haka kuma, ministan ya ce Ghana ta ci gajiyar hadin gwiwar kasashen biyu a fannonin ababen more rayuwa da ilimi da tsaro da aikin gona da sadarwa da kiwon kifi. (Fa’iza Mustapha)