logo

HAUSA

An Yi Kira Da A Ingiza Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ta Kudu Zuwa Sabon Matsayi

2023-08-23 16:58:11 CMG Hausa

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana jiya Talata a birnin Pretoria cewa, yana son yin aiki tare da takwaransa na kasar Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, wajen ciyar da dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Afirka ta Kudu zuwa wani sabon mataki.