logo

HAUSA

Umar Ilyasu Sani: Ina son kara fadakar da al’ummar Najeriya kan kasar Sin

2023-06-06 15:43:59 CMG Hausa

Umar Ilyasu Sani, dan asalin jihar Kanon tarayyar Najeriya ne, wanda a yanzu haka yake karatu a kwalejin koyon ilimin kasuwanci dake birnin Shanghai na kasar Sin.

A zantawar sa da Murtala Zhang, malam Umar Ilyasu Sani, ya bayyana abubuwan da suka burge shi a kasar Sin, musamman birnin Shanghai, da bambancin yanayin karatu tsakanin Najeriya da kasar Sin a ra’ayinsa.

Malam Umar ya kuma bayar da shawarwari ga daliban Najeriya, wadanda ke son zuwa kasar Sin don yin karatu. (Murtala Zhang)