logo

HAUSA

An kaddamar da shirin kula da lafiyar marayu na Afirka

2023-06-02 16:03:24 CMG Hausa

A gabannin ranar yara ta duniya ta ranar 1 ga watan Yuni, Peng Liyuan, mai dakin shugaban kasar Sin Xi Jinping, da kungiyar  masu dakin shugabannin kasashen Afirka ta neman samun bunkasuwa, sun kaddamar da wani shirin hadin gwiwa, da zai taba zukatan yara marayu na kasashen Afirka. Ofisoshin jakadancin kasar Sin dake kasashen Afirka da tawagogin likitocin dake kasashen da abin ya shafa, sun ziyarci kananan yara a gidajen kula da marayu ko cibiyoyin da ke da alaka da su, inda suka gudanar da aikin duba lafiyarsu kyauta, tare da ba da gudummawar kunshin kayayyaki da dai sauransu.