logo

HAUSA

Xi ya tashi zuwa kasar Sin bayan ziyarar aiki da ya kai kasar Rasha

2023-03-22 16:14:44 CMG Hausa

Da safiyar Larabar nan ce, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tashi zuwa kasar Sin, bayan kammala ziyarar aiki da ya kai kasar Rasha.

Kafin tashin Xi, mataimakin firaministan kasar Rasha Dmitry Chernyshenko, da wasu manyan jami'an Rasha sun shirya masa kasaitaccen bikin ban kwana a filin jirgin sama. (Ibrahim Yaya)