logo

HAUSA

Zamanintarwa irin na kasar Sin za ta amfana wa duniya

2023-03-13 09:22:29 CMG Hausa

Yanzu haka ana gudanar da manyan taruka biyu na kasar Sin wato babban taron majalisar wakilan jama’ar kasar da babban taron majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar, wannan shi ne karo na farko da aka kira tarukan biyu, tun bayan da da aka kammala babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 20 a shekarar bara, inda aka fi mai da hankali kan yadda za a ingiza aikin zamanintarwa irin na kasar Sin.