An sako mata da yara sama da 60 da aka sace a Burkina Faso
2023-01-22 17:21:25 CMG Hausa
Rundunar sojin Burkina Faso, ta ceto mata da yara 66 da aka sace a farkon watan nan, a yankin Sahel na kasar.
Wasu ‘yan bidiga da ba a san ko su wanene ba ne suka sace matan, cikin su har da jarirai 4, a tsakanin ranakun 12 da 13 ga wannan wata, a kusa da garin Arbinda na yankin.
Gidan talabijin na RTB na kasar ya ruwaito cewa, wani samamen dakarun tsaro ne ya kai ga ceto su a ranar Juma’ar da ta gabata a yankin arewa maso tsakiyar kasar, inda aka kai su birnin Ouagadougou. (Fa’iza Mustapha)