logo

HAUSA

Masu garkuwa da mutane sun yi awon gaba da mutane a kalla 60 a jihar Zamfara

2022-11-25 14:25:38 CMG Hausa

Rahotanni daga jihar Zamfara dake arewa maso yammacin Najeriya na cewa, masu garkuwa da mutane sun sace wasu mutane a kalla 60 a jihar, lokacin da suke halartar taron Mauludi.

Shaidu daga yankin sun tabbatar da aukuwar al’amarin a jiya Alhamis, a wani yanayi mai muni, na sake yin garkuwa da mutane da jihar ta jima tana fama da shi.  (Saminu Alhassan)