Shugabar kasar Tanzania za ta ziyarci kasar Sin
2022-10-27 13:55:23 CMG Hausa
Bisa gayyatar shugaban kasar Sin Xi Jinping, shugabar kasar Tanzania Samia Suluhu Hassan za ta kawo ziyara kasar Sin tsakanin ranekun 2 zuwa 4 ga watan Nuwamba mai zuwa, kamar dai yadda kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Hua Chunying ta bayyana a yau Alhamis. (Saminu Alhassan)