Xi ya jaddada yin nazari, fahimta da aiwatar da muhimman ruhin babban taron JKS
2022-10-26 14:32:26 CMG Hausa
Babban sakataren kwamitin kolin JKS Xi Jinping, ya jadadda bukatar cikakken yin nazari da fahimta da kuma aiwatar da ka’idojin babban taron wakilan JKS na 20, domin ganin an cimma sabbin nasarori a kokarin da ake na gina kasar Sin ta zamani mai bin sigar gurguzu a dukkan fannoni.
Xi ya bayyana haka ne, lokacin da ya jagoranci taron nazari na farko na ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS karo na 20. (Ibrahim)