Za a gudanar da babban taron wakilan JKS karo na 20 a ranar 16 ga wata
2022-10-14 20:28:09 CMG Hausa
A safiyar ranar 16 ga wata da misalin karfe 10 ne, za a gudanar da babban taron wakilan JKS karo na 20, a babban dakin taron jama’a dake birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.
A yayin taron, babban rukunin gidan rediyo da talabijin na kasar Sin (CMG) da Xinhuanet, za su watsa abubuwan dake gudana kai tsaye. (Ibrahim)