Majalisar CPC karo na 20 za ta gudanar da taron manema labarai ranar Asabar
2022-10-11 18:50:13 CMG Hausa
Mai magana da yawun babban taron wakilan JKS karo na 20, zai gudanar da taron manema labarai a babban dakin taron jama’a dake birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin a ranar 15 ga watan Oktoban wannan shekara.
‘Yan jaridu za su iya halartar taron a wani karamin wuri da aka kafa a zauren karni dake hawa na 3 a otel din Nikko New Century dake birnin na Beijing. (Ibrahim)