logo

HAUSA

Najeriya ta ce sojojinta sun kashe mayakan IS da dama

2021-11-29 20:15:18 CRI

Mai magana da yawun rundunar sojojin Najeriya Onyema Nwachukwu, ya bayyana cewa, sojojin kasar sun yi nasarar kashe mayakan kungiyar IS ta yammacin Afirka (ISWAP) da dama, yayin da suka kai hari a wani sansanin soji a jihar Borno da ke arewa maso gabashin kasar.

Wata sanaewa da Onyema Nwachukwu ya fitar na cewa, sojoji biyu ne suka mutu sakamakon harin da kungiyar ISWAP ta kai a ranar Lahadi a sansanin sojojin da ke karamar hukumar Gajiram Nganzai a jihar Borno.

Ya bayyana cewa, ayarin jiragen sama na Operation Hadin Kai, dake daukar matakan soja a yankin arewa maso gabashin kasar, ya yi barin wuta kan ‘yan ta’addan da suka yi yunkurin kutsawa cikin sansanin. (Ibrahim)

Ibrahim