logo

HAUSA

Xi zai halarci taron kolin CPC da jam’iyyun siyasun duniya

2021-07-05 10:02:09 CRI

Mai magana da yawun sashen harkokin cudanya a tsakanin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin da kasashen waje na kwamitin tsakiya na JKS Hu Zhaoming, ya sanar Litinin din cewa, babban sakataren kwamitin tsakiya na JKS Xi Jinping, zai halarci taron kolin JKS da jam’iyyun siyasu na duniya da za a gudanar ta kafar bidiyo.

Xi Jinping zai halarci taron ne daga nan birnin Beijing, tare da gabatar da muhimmin jawabi. (Ibrahim)