Namibia za ta karbi rancen dala miliyan 100 daga bankin AfDB
2021-03-25 10:28:48 CRI
Kasar Namibia za ta karbi rancen dalar Amurka miliyan 100 daga bankin raya Afrika na AfDB, domin taimakawa ayyukan shugabanci da farfado da tattalin arziki.
Kakakin ma’aikatar kudi ta kasar Tonateni Shidhudhu, ya bayyana cikin wata sanarwa cewa, bukatar da aka gabatarwa bankin AfDB a watan Yunin shekarar 2020, ya samu amincewar daukacin mambobin hukumar daraktocin bankin a ranar 17 ga wata a shekarar 2021 da muka ciki, a matsayin rancen kudin aiwatar da harkokin shugabanci da shirin farfado da tattalin arzikin kasar.
Ya ce an amince da bayar da rancen ne bayan kammalawar shirin raya tattalin arziki da ya gudana tsakanin shekarar 2017 zuwa 2020, wanda ya samu dimbin sakamako a bangarorin rage gibin kudi da basussukan gwamnati da tafiyar da dukiyar al’umma da inganta yanayin kasuwanci. Sai dai, annobar COVID-19 na barazanar mayar da hannun agogo baya. (Fa’iza Mustapha)
Labarai Masu Nasaba
- Namibia ta kaddamar da aikin bayar rigakafin COVID-19 da Sin ta ba ta gudunmuwarsu
- Namibia ta bude tallar neman wadanda za su iya samar mata alluran COVID-19
- Namibia ta amince da yarjejeniyar kafa hukumar sa ido kan magunguna ta Afrika
- Kasar Sin za ta bada gudunmuwar alluran riga kafi 100,000 ga kasar Namibia