An Kaddamar Da Harkokin Murnar Bikin Bazara Na Kasar Sin Kan Intanet
2021-02-04 19:26:58 CRI
Yau Alhamis 4 ga wata ne aka kaddamar da harkokin murnar bikin Bazara bisa kalandar gargajiyar kasar Sin ta kafar yanar gizo ko Intanet a nan birnin Beijing. Ministan al’adu da aikin yawon shakatawa na kasar Sin Hu Heping, da shugaban babban gidan rediyo da talibijin na kasar Sin na CMG Shen Haixiong, sun ba da nasu jawabai ta kafar bidiyo don kaddamar da harkokin.
Wadannan harkoki sun hada da masu halin musamman na bikin Bazara, wadanda suka shafi al’adun kasar Sin, da harkokin kara fahimtar al’adu da aikin bude ido, da wasanni masu kayatarwa, da masu fasaha na gida da wajen kasar Sin za su nuna, ta yadda ’yan kallo daga sassa daban daban na duniya za su kara fahimtar bikin Bazara, duk da suna cikin gidajensu. (Tasallah Yuan)
Labarai Masu Nasaba
- CMG ta kaddamar da gwajin fasahar 8K a tashar talabijin
- CMG ta kaddamar da shirin tallata hajojin lardin Hubei na shekarar 2021
- Shugaban CMG ya yi kira ga kafafen yada labaran yamma su gyara kurakurensu na jirkita gaskiyar labaran da suka shafi kasasr Sin
- Jawabin Shugaban CMG Na Murnar Sabuwar Shekarar 2021 Ga Masu Sauraro Da Masu Kallo