Ranar 21 ga watan Satumba, 'yan ta'adda sun kai hari kan babban shagon Westgate Mall da ke birnin Nairobi, hedkwatar kasar Kenya, inda mutane 67 suka rasa rayukansu, yayin da mutane fiye da 170 suka jikkata. Bisa adadin da kungiyar ba da agaji ta Red Cross ta kasar ta gabatar, an ce, akalla mutane 39 sun bace sakamakon harin.