in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na fatan sassa daban daban na Gambiya za su hada kansu don kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasarsu
2017-01-23 18:52:50 cri

Yau Litinin ne, madam Hua Chunying, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta yi maraba da warware rikicin kasar Gambiya cikin lumana, ta kuma yi fatan cewa, sassa daban daban na kasar za su ba da muhimmanci ga muradun kasa da ta jama'arsu, za su kuma hada kai wajen kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar da himmantuwa wajen farfado da kasar.

Rahotanni na cewa, MDD, AU, da ECOWAS sun ba da wata sanarwar hadin gwiwa, inda suka bayyan aniyarsu ta yin aiki da sabon shugaban Gambiya mista Adama Barrow. Tuni dai, dakarun sojan hadin gwiwar kasashen yammacin Afirka suka shiga kasar ta Gambiya, a kokarin tabbatar da ganin mista Adama Barrow ya koma kasar ya kama aiki lami lafiya. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China