A yau Litginin ne Geng Shuang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya yi tir da babbar murya kan hare-haren ta'addanci da aka kaddamar a biranen Istanbul da Alkahira a kwanan baya, ya kuma jajantawa iyalan wadanda suka rasa rayukansu da kuma wadanda suka jikkata sakamakon hare-haren.
Ya kara da cewa, kasar Sin tana Allah-wadai da duk wani nau'in ta'addanci, kana tana son ci gaba da goyon bayan kokarin da kasashe masu ruwa da tsaki suke bayarwa wajen tabbatar da kwanciyar hankali da tsaro da kuma yaki da ta'addanci. (Tasallah Yuan)