in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An tabbatar da asalin mutumin da ya kai harin birnin Nice na Faransa
2016-07-15 20:20:57 cri
Rahotanni daga kasar Faransa na cewa, 'yan sandan kasar sun tabbatar da asalin direban da ya kai hari da motar daukan kaya inda ya kutsa kai cikin taron jama'a dake kallon wasan wuta albarkacin bikin ranar samun 'yanci a birnin Nice dake kudancin Faransa a daren ranar jiya 14 ga wata.

An gano asalin maharin ne ta hanyar tantance hoton zanen yatsunsa, wanda kuma ya dace da takardar shaidar da aka samu cikin motar da ya ke tukawa.

Direban motar dan kasar Faransa ne mai shekaru 31, kuma an haife shi a kasar Tunisiya, amma yana zaune ne a birnin Nice, haka kuma, 'yan sandan kasar Faransa sun taba kama shi bisa laifin mallakar bindigogi da kuma aikata laifin tayar da hankali da kuma sata, amma ba a taba gabatar batun nasa ga hukumar leken asirin kasar ta Faransa ba.

A jiya Alhamis da dare ne, wata motar daukan kaya ta kutsa kai cikin taron jama'a dake kallon wasan wuta albarkacin bikin ranar samun 'yancin kai a birnin Nice dake kudancin Faransa, lamarin da ya haddasa mutuwar mutane 84, yayin da 50 suka jikkata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China