in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya mika sakon alhini ga takwaransa na Faransa
2016-07-15 16:15:55 cri
Yau Jumma'a 15 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya mika sakon alhini ga takwaransa na kasar Faransa Francois Hollande kan harin da aka kai a kasar, inda ya kuma yi Allah wadai da wannan danyen aiki da aka aikata, tare da nuna juyayi matuka ga wadanda suka rasa rayukansu cikin wannan hari, ya kuma nuna jajantawa ga wadanda suka jikkata.

Bugu da kari, Xi Jinping ya ce, ta'addanci ya kasance wani babban kalubale dake gaban al'ummomin kasa da kasa, kasar Sin tana tsayawa tsayin daka wajen yaki da dukkan nau'o'in ta'addanci, tana kuma goyon bayan kasar Faransa wajen kiyaye tsaron kasarta, shi ya sa, kasar Sin tana son karfafa hadin gwiwa tare da kasar Faransa a wannan fanni, domin kiyaye tsaron kasashen biyu, da na kasashen duniya baki daya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China