in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Magajin birnin Mbalmayo ya baiwa tawagar likitancin Sin lambar yabo
2016-06-04 17:16:22 cri
Jiya Jumma'a 3 ga wata, magajin birnin Mbalmayo malam Oberer dake yankin tsakiyar kasar Kamaru ya mika lambar yabo game da muhimmiyar gudummawar da tawagar likitancin kasar Sin ta bayar a wannan kasa.

A yayin bikin, Mr. Oberer ya ce, ya mika lambar yabo din ga tawagar likitanci ta Sin a madadin gwamnatin kasar Kamaru, domin nuna mata yabo kan babban taimakon da ta samar wa asibitin Mbalmayo, haka kuma, ya yi godiya ga gwamnatin kasar Sin kan taimakon da Sin ta baiwa kasar Kamaru a fannin likitanci, da kuma babban gudummawa da kasar Sin ta bayar wajen kyautata yanayin kiwon lafiyar al'ummomin birnin, haka kuma, al'ummominsa za su ci gaba da nuna godiya kan taimakon da suka samu a ko da yaushe. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China