in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kafar watsa labaran Kamaru ta yabawa kasar Sin game da taimakawa Afirka
2016-03-11 11:25:38 cri
Babbar kafar watsa labarai ta jamhuriyar Kamaru wato Cameroon Tribune, ta fidda rahoto game da bayanin da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi, game da manufofin diflomasiyyar kasar Sin da dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen ketare, inda ya yabawa yadda kasar Sin ke taimakawa kasashen Afirka.

Rahoton ya tabo batun manyan shirye-shiryen hadin gwiwa 10 dake tsakanin Sin da Afirka, inda ya bayyana cewa, ko da ana samun yanayi maras kyau wajen raya tattalin arzikin duniya a halin yanzu, amma kasar Sin ta jaddada cewa, za ta ci gaba da taimakawa kasashen Afrika wajen aiwatar da muhimman ayyuka, kuma babban burin kasar Sin wajen fitar da manyan harkokin hadin gwiwar 10 a yayin taron dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka da aka yi a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu a watan Disambar shekarar 2015 shi ne, domin taimakawa kasashen Afirka wajen kawar da talauci, da kuma cin moriyar juna.

Bugu da kari, rahoton ya bayyana cewa, bayan da aka kammala taron, ba tare da bata lokaci ba, kasar Sin ta fara yin shawarwari tare da kasashen Afirka da abin ya shafa, domin aiwatar da shirin yadda ya kamata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China