in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamaru ta shirya taron tattalin arziki na kasa da kasa don jawo jari daga kasashen waje
2016-05-18 09:46:07 cri
A jiya ne a cibiyar taro na kasa da kasa da ke birnin Yaounde hedkwatar kasar Kamaru aka kaddamar da taron tattalin arziki na kasa da kasa da gwamnatin Kamaru ta shirya.

Makasudin shirya taron mai taken "Saka jari a kasar Kamaru, kasa mai dama", shi ne a baiwa masu saka jari na kasashen waje damar raya tattalin arziki da Kamaru take da shi, gami da damar saka jari.

A jawabinsa yayin bikin bude taron, shugaban kasar Kamaru Paul Biya ya bayyana cewa, Kamaru na da fiffiko a wasu fannoni da dama wadanda za a saka jari a ckinsu, baya ga albarkar kasa mai kyau, da albarkatun ma'adinai, da yanayi, da yankunan kasa, kuma dukkan wadannan suna taimakawa aikin gona a wurin. Ban da wannan kuma, tashar jiragen ruwa, da filin jiragen sama, da hanyoyin jiragen kasa da na mota da sauran muhimman ababen more rayuwa sun taimakawa aikin raya yankunan da ciniki tsakanin kasa da kasa.

Wakilan kasashen duniya sama da 500 ne suka halarci taron da za a shafe kwanaki 2 ana yinsa, inda tsohon shugaban hukumar zartarwar kungiyar EU José Manuel Durão Barroso da tsohon firaministan kasar Koriya ta Kudu CHUNG UN-CHAN sun yi jawabi a yayin bikin bude taron.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China