in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Kamaru na ziyarar aiki a Najeriya kafin wani taron shiyya-shiyya kan Boko Haram
2016-05-04 10:04:50 cri
Shugaban kasar Kamaru Paul Biya ya fara wata ziyarar aiki ta kwanaki biyu a jiya Talata a tarayyar Najeriya, makwanni biyu da suka rage kafin bude taron shiyya-shiyya kan yaki da kungiyar Boko Haram da aka tsaida a ranakun 14 da 15 ga watan Mayu a birnin Abuja, tare da shugaban kasar Faransa Francois Hollande.

Tare da rakiyar mambobin gwamnatinsa da ba'a bayyana sunanyensu ba da farko da kuma matarsa Chantal, shugaban kasar Kamaru ya bar birnin Yaounde kafin misalin karfe goma na safe bisa agogon wurin zuwa babban birnin Najeriya, inda ya samu babban tarbo daga takwaransa Muhammadu Buhari.

Wannan shi ne karo na biyu da shugabannin kasashen biyu suke ganawa a tsawon kusan shekara daya bayan ganarwarsu ta farko a yayin ziyarar shugaba Buhari a birnin Yaounde a ranakun 29 da 30 ga watan Yulin shekarar 2015, watanni biyu bayan kama aiki a matsayin sabon shugaban Najeriya, kasa ta farko a fuskar tattalin arziki a yammacin Afrika bayan nasarar kan shugaba mai barin gado Goodluck Jonathan a zaben shugaban kasa na ranar 29 ga watan Maris. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China