in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Kamaru yana son ci gaba da zurfafa hadin gwiwa dake tsakanin kasarsa da kasar Sin
2015-01-08 14:53:02 cri
Yayin da shugaban kasar Kamaru Paul Biya yake karbar takardun nadin sabon jakadan Sin Wei Wenhua da Sin ta tura zuwa Kamaru a ranar 6 ga wata, ya bayyana cewa, kasar Kamaru tana godiya ga kasar Sin kan goyon baya da gudummawar da take baiwa kasar a fannonin bunkasuwar tattalin arziki da zamantakewar al'umma, kana yana fatan za a ci gaba da zurfafa hadin gwiwar da ke tsakaninsu

Hakazalika shugaba Biya ya yaba da manyan nasarori da kasar Sin ta samu lokacin da ta fara aiwatar da manufar bude kofa da yin kwaskwarima, kuma ya yaba da dangantakar hadin gwiwa dake tsakanin kasashen biyu.

A nasa bangare, jakada Wei Wenhua ya bayyana cewa, kasashen Sin da Kamaru na sada zumunta tsakaninsu, sannan suna hadin gwiwa a fannonin siyasa, tattalin arziki, cinikayya, al'adu da sauransu tun bayan da suka kulla dangantakar diplomasiyya a tsakaninsu.

Kuma kasar Sin tana son yin kokari tare da kasar Kamaru wajen kara yin mu'amala a tsakanin al'ummomin kasashen biyu, da zurfafa hadin gwiwar don inganta dangantakar da ke tsakaninsu zuwa wani sabon matsayi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China