in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Kamaru zai kai ziyarar aiki ta kwanaki uku a Najieriya tun daga yau ranar Talata
2016-05-03 09:25:55 cri
Shugaban kasar Kamaru Paul Biya zai kai wata ziyarar aiki ta kwanaki uku a kasar Najeriya tun daga yau ranar Talata, ta farko tun bayan zaben takwaransa Muhammadu Buhari a cikin watan Maris din shekarar 2015, a cewar wata sanarwar fadar shugaban kasar Kamaru da aka fitar a ranar Litinin.

Koda yake sanarwar ba ta bayyana makasudin ziyarar ba, amma ana ganin cewa musanyar tsakanin shugabannin biyu za ta mai da hankali kan yaki da kungiyar Boko Haram da kasashen biyu suke gudanarwa a cikin rundunar hadin gwiwa da kwamitin tafkin Chadi (CBLT) ya kafa da kuma kasashen biyu suke mamba.

A cikin watan Yulin shekarar 2015, kimanin watanni biyu bayan rantsar da shi a karshen watan Mayu a birnin Abuja, mista Buhari ya kai irin wannan ziyarar aiki a birnin Yaounde tare da wannnan muhimmin batun yaki da Boko Haram. Tun lokacin, Yaounde da Abuja suka karfafa dangantaka, musammun ma a fannin yaki da ta'addanci. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China