in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi yana son karfafa goyon baya da sada zumunta a tsakanin Sin da Afirka
2015-01-14 10:42:07 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya kai ziyara a kwalejin Confucius dake jami'a ta biyu ta birnin Yaoundé na kasar Kamaru tare da ministan harkokin wajen kasar Kamaru Pierre Moukoko Mbonjo da ministan kula da harkokin ilmin jami'a na kasar Jacques Fame Ndongo a ranar 13 ga wata, inda malamai da dalibai a kwalejin suka nuna maraba da zuwansa.

Wang Yi ya bayyana cewa, kwalejin Confucius na tamkar wata gadar dake sada zumunta a tsakanin Sin da Afirka.

Haka kuma, Wang Yi ya kara da cewa, kamata ya yi Sin ta ci gaba da yin kokari, ta yadda matasa a kasar Kamaru zasu yi imanin cewa, kasar Sin wata babbar kasa ce dake daukar alhakin kanta da sada zumunta da yin kokarin samun bunkasuwa tare da abokanta na Afirka. Don haka, ya kamata kowane mutum ya zama mai goyon baya da sada zumunta a tsakanin Sin da Afirka, da kuma yin kokari tare a wannan fanni. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China