in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Mozambique ya gana da ministan harkokin wajen kasar Sin
2016-02-03 15:38:28 cri
Shugaban kasar Mozambique Filipe Nyusi ya gana da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi a fadar sa a ranar Talata. Yayin ganawar tasu, Mista Nyusi ya ce, Mozambique na fatan hadin gwiwa da kasar Sin a fannoni daban-daban, ciki hadda na makamashi, da sha'anin samar da kayayyaki, da manyan ababen more rayuwa, da sha'anin gona, da tsaro da dai sauransu, don jama'ar kasar su ci gajiya daga alakar sassan biyu.

Ya ce shugabannin kasashen Afrika na yabawa da shirye-shiryen zurfafa hadin gwiwa tsakanin Sin da Afrika guda goma, wadanda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar ga taron koli na Johannesburg, na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afrika.

A nasa bangare, Mista Wang ya ce wadannan shirye-shirye da shugaba Xi ya gabatar sun dace da moriyar nahiyar Afrika na raya kansu, kuma su na da ma'ana sosai wajen kara karfin bunkasa kasashen Afrika wajen dogaro da kansu, da karfin tinkarar kalubaloli daga kasashen waje. Ya ce ana fatan kara hadin gwiwa da kasar Mozambique ta fuskar karfin samar da kayayyaki, da sha'anin gona, ta yadda za a kafa wani cikakken tsari na samar da hatsi a Mozambique, sannan kuma a zurfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu ta fuskar zaman lafiya da tsaro. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China