in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dan takarar jam'iyyar dake mulki a kasar Mozambique Filipe Nyusi ya ci babban zaben kasar
2014-10-31 15:57:52 cri
An gabatar da sakamakon babban zaben kasar Mozambique a ranar 30 ga wata, inda dan takarar jam'iyyar Frelimo dake kan karagar mulkin kasar Filipe Nyusi ya samu kuri'u na kashi 57.03 cikin dari wanda ya ba shi damar zama shugaban kasar na hudu bayan da kasar ta samu 'yancin kai. Haka kuma jam'iyyarsa ta lashe zaben majalisar dokokin kasar da na kananan hukumomi.

Bisa sakamakon da hukumar zaben kasar Mozambique ta gabatar a birnin Maputo a wannan rana, an ce, dan takara na jam'iyyar Renamo, Afonso Dhlakama ya samu kuri'u na kashi 36.61 cikin dari, kuma dan takara na jam'iyyar MDM, Daviz Simango ya samu kuri'u na kashi 6.36 cikin dari.

Haka kuma cikin kujeru 250 na majalisar dokokin kasar, jam'iyyar Frelimo ta samu kujeru 144, adadin da ya ragu da 47 bisa na majalisar da ta gabata. Yawan kujerun da jam'iyyar Renamo ta samu a majalisar dokokin kasar a wannan karo ya karu da 38 inda ya kai 89. Kuma yawan kujerun mallakar jam'iyyar MDM ya karu daga 8 zuwa 17.

Kafin a gabatar da sakamakon zaben, shugaban hukumar zaben kasar Abdul Carimo ya bayyana wasu ayyukan da suka sabawa ka'idojin zaben, kuma ya ce ana yin bincike kansu

Bayan da aka gabatar da sakamakon kwarya-kwarya a ranar 18 ga wata, jagoran jam'iyyar Renamo Dhlakama yayi zargin cewa an tabuka magudi yayin zabe, tare da yin watsi da sakamakon zaben. Sai dai jam'iyyar Frelimo ta ki amince da zargin jam'iyyar Renamo.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China