in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Mozambique da 'yan adawa sun daddale yarjejeniyar tsagaita bude wuta
2014-08-25 10:44:22 cri
Mahukuntan kasar Mozambique da wakilan jam'iyyar Renamo ta 'yan adawa, sun cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta a daren jiya Lahadi. Shugaban tawagar wakilan gwamnatin kasar Jose Pacheso, wanda ya wakilci shugaban kasar Armando Guebuza, da shugaban tawagar wakilan jam'iyyar ta Renamo Saimone Macuiana, da ya wakilci shugaban jam'iyyar Afonso Dhlakama ne suka rattaba hannu, kan yarjejeniyar a birnin Maputo fadar mulkin kasar.

Baya ga wakilan tsagin biyu, an kuma gayyaci wasu 'yan kallo daga fannin ayyukan soja na kasashen waje, domin taimakawa mayakan jam'iyyar Rename a aikin kawar da makamai, da shigar da su cikin rundunar sojojin tsaron kasar.

Game da yarjejeniyar da aka kulla, shugaban tawagar wakilan jam'iyyar ta Renamo ya ce, dakarun jam'iyyarsa, za su dakatar da daukar dukkanin wani mataki na nuna kiyyaya ga gwamnatin kasar. Ya ce yarjejeniyar tsagaita bude wutar da suka shiga da gwamnatin kasar ta shaida matakin da Mozambique ta dauka, na bude sabon shafin samun bunkasuwa, wanda ke wakiltar kyakkyawan fatan jama'ar kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China