in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'an AU sun nuna yabo game da taimakon Sin wajen gina ababen more rayuwa a Afirka
2016-01-31 13:21:15 cri
A ran 29 ga wata, wato jajibirin gudanarwar taron shugabannin kungiyar tarayyar kasashen Afirka AU karo na 26 a babban birnin kasar Habasha, Addis Ababa, mamban kwamitin kula da harkokin ababen more rayuwa da makamashi na kungiyar AU, mista Elham M.A.Ibrahim ya bayyana cewa, kasar Sin ta ba da taimako matuka ga kasashen Afirka wajen kyautata yanayin ababen more rayuwa ta hanyoyin zuba jari a nahiyar wajen gina hanyoyin mota, tashoshin jiragen ruwa da dai sauransu.

Haka kuma, ya ce, kasar Sin tana amfani da fasahohin zamani wajen gina ababen more rayuwa a nahiyar Afirka, hakan ya sa, an gina kayayyaki masu inganci matuka kuma cikin sauri, lamarin da ya taimaka wa kasashen Afirka matuka wajen samun ababen more rayuwa masu zamani. A halin yanzu kuma, kungiyar AU da kasar Sin suna tattaunawa kan karfafa hadin gwiwa da mu'amalar dake tsakaninsu, domin aiwatar da sakamakon da aka samu cikin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka da aka yi a karshen shekarar da ta gabata a kasar Afika ta Kudu.

Bugu da kari, malam Ibrahim ya nuna cewa, kungiyar AU na gudanar da harkokin jadawalin shekarar 2063 yadda ya kamata, wanda yake mai da hankali kan kyautata yanayin ababen more rayuwa na zamani a kasashen Afirka, domin raya harkokin ciniki da masana'antu na mambobin kungiyar AU, da kuma ciyar da dunkulewar kasashen Afirka gaba yadda ya kamata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China