in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin AU ya nuna godiya ga Sin kan goyon bayan da ta samar wajen gina cibiyar shawo kan cututtuka ta Afirka
2015-07-22 16:36:09 cri
Mataimakin shugaban kwamitin kungiyar tarayyar kasashen AU Erastus Mwencha ya bayyana a ran 21 ga wata cewa, kasar Sin ta ba da gudummawa wajen gina cibiyar shawo kan cututtuka ta Afirka, haka kuma, kungiyar AU na son ci gaba da karfafa hadin gwiwar dake tsakaninta da kasar Sin a fannonin da suka shafi bada jinya da magunguna.

A yayin wani zaman taro kan yaki da cutar Ebola a Afirka wanda aka kammala a ran 21 ga wata, Mr. Mwencha ya bayyana cewa, kasar Sin ta samar da taimako matuka ga gina cibiyar shawo kan cututtuka ta Afirka a fannonin ba da horo ga ma'aikatanta, koyar musu fasahohin tafiyar da ayyuka da kuma samar mata da kudade. Bugu da kari, ya kuma nuna godiya sosai ga kasar Sin kan taimakon da ta samar wa kasashen da suka yi fama da cutar Ebola kan hanyoyin yaki da cutar da kuma sake gina wadannan kasashe. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China