in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kuang Weilin:Ana kokarin ba da gudummawa ga sa kaimi ga raya dangantaka tsakanin Sin da kasashen Afirka
2016-01-30 13:11:00 cri
Za a kaddamar da taron shugabannin kungiyar tarayyar kasashen Afirka (AU) karo na 26 a birnin Addis Ababa a yau Asabar 30 ga wata.

A game da hakan, shugaban tawagar Sin a kungiyar AU na farko, mista Kuang Weilin ya bayyana cewa, tawagar za ta kara kokarin sa kaimi ga tabbatar da sakamakon da aka samu a taron kolin Johannesburg na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka, ta yadda za ta kara ba da gudummawa ga raya dangantaka tsakanin Sin da kasashen Afirka.

Tawagar Sin a kungiyar AU ta fara aiki ne a watan Maris na bara a hukunce kamar yadda Mista Kuang ya gaya wa wakilinmu, kafa wannan tawaga na da ma'ana sosai, wadda ta bayyana cewa, dangantaka tsakanin Sin da nahiyar Afirka, da dangantaka tsakanin Sin da kungiyar AU, dukkansu sun shiga wani sabon mataki.

Ban da haka, mista Kuang ya jaddada cewa, wannan ne karo na farko da aka kira taron kolin kungiyar AU bayan taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka shirya a Johannesburg a watan Disamban bara. Shugaban kasar Sin Xi Jinping a jawabinsa a gun taron kolin Johannesburg, ya fitar da manyan ginshikai biyar da shirye shirye 10 na yin hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka. Hakan ya nuna alkibla ga bunkasuwar dangantaka tsakanin Sin da nahiyar Afirka, da kuma bunkasuwar dangantaka tsakanin Sin da kungiyar AU baki daya.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China