in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musaman na gwamnatin kasar Sin Zhang Ming ya gana da shugabar kwamitin kungiyar AU
2016-01-29 10:47:03 cri
Manzon musamman na gwamnatin kasar Sin kana mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Zhang Ming ya gana da shugabar hukumar zartarwar kungiyar AU Dlamini-Zuma a yayin taron koli na kungiyar AU karo na 26 da aka gudanar a birnin Addis Ababa na kasar Habasha a jiya Alhamis 28 ga wata.

A yayin ganawar, Zhang Ming ya bayyana cewa, an raya dangantakar dake tsakanin Sin da kungiyar AU a shekarar 2015. A yayin taron koli na dandalin tattaunawa kan hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka a birnin Johannesburg a watan Disamba na shekarar bara, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugabar kwamitin kungiyar AU Dlamini-Zuma, inda suka tabbatar da makomar dangantakar dake tsakanin Sin da kungiyar AU, da samar da gudummawa don raya dangantakar dake tsakaninsu. Kasar Sin za ta yi amfani da sakamakon taron koli na Johannesburg don aiwatar da yarjejeniyar da shugaba Xi Jinping da shugaba Zuma suka cimma daidaito a kai, da kuma sa kaimi ga raya dangantakar dake tsakanin Sin da kungiyar AU da kuma dangantakar abokantaka a tsakanin Sin da Afirka yadda ya kamata.

A nata bangare, Madam Zuma ta nuna godiya ga shugaba Xi Jinping bisa ga shawarwarin da ya bayar a taron koli na Johannesburg. Ta kuma marabci Zhang Ming a taron kungiyar AU. Zuma ta yabawa kasar Sin a kokarin da take na raya dangantakar dake tsakaninta da kasashen Afirka da kungiyar AU, kungiyar AU tana son hada kai tare da kasar Sin don zurfafa hadin gwiwarsu a fannonin jiragen kasa da na sama, hanyoyin mota, masana'antu, aikin gona, da kuma kiyaye tsaro, ta yadda za su samu moriyar juna da bunkasuwa tare. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China