in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi matukar Allah wadai da harin da aka kai jami'ar Moi dake Kenya
2015-04-03 21:17:51 cri

Kasar Sin ta kakkausa murya wajen yin Allah-wadai, da harin da aka kai jami'ar Moi da ke garin Garissa na kasar Kenya, harin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 147, a cewar madam Hua Chunying, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar ta Sin.

Madam Hua ta bayyana haka ne a yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa. Ta kuma mika sakon ta'aziyya ga wadanda suka rasa rayukansu yayin harin, tare da jajantawa iyalan mamatan, da kuma wadanda suka jikkata sakamakon harin.

Kakakin ta jaddada cewa, kasar Sin za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka, wajen mara wa Kenya baya, a kokarinta na kiyaye tsaron kasa, da kuma wanzar da yanayin zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin da take baki daya. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China