in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yan sandan Nigeriya sun kame mutane 67 da laifuffuka lokacin zabe
2015-04-03 10:25:27 cri
Yan sandan Nigeriya na jihar Kano sun tabbatar da kame wadansu mutane da ake zargin sun aikata laifuffukan da suka shafi babban zaben kasar da aka kammala karshen mako na shugaban kasa da 'yan majalissar tarayya.

Kakakin rundunar 'yan sandan Magaji Majiya ya sanar wa manema labarai Alhamis din nan cewa, an kame wadanda ake zargin ne a sassa daban daban na jihar, da aika abin da ya saba wa ka'idojin zabe na son tada zaune tsaye da kwace akwatunan zaben.

Malam Magaji Majiya ya ce, wadansun su ma an same su dauke da makamai, kamar su kwari da baka, wukake, takubba, sanduna da adda, sai dai ya jinjina wa al'ummar jihar bisa ga hadin kan da suka bayar ga hukumar 'yan sandan a lokacin zaben, abin da ya sa aka samu nasarar kammala zaben cikin lumana da kwanciyar hankali.

Ya kara da cewa, su ma 'yan sanda a nasu bangaren sun nuna kwarewarsu na aiki matuka wajen tabbatar da an bi doka da oda yadda tsarin mulki ya tanada musu a lokacin zaben.

Daga nan sai ya yi kira ga daukacin 'yan Nigeriya musamman matasa da su yi taka tsantsan a kan yadda suke nuna murnarsu ta nasarar da Muhammadu Buhari ya yi domin kauce wa wassu tsautsayi. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China