in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musamman na MDD mai kula da harkokin ilmi ya yi kira da a tabbatar da tsaron makarantun dake yankuna masu fama da rikice-rikice
2015-03-19 10:23:48 cri
Manzon musamman na MDD mai kula da harkokin ilmi a duniya kuma tsohon firaministan kasar Britaniya Gordon Brown ya bayyana a ranar 18 ga wata cewa, yawan hare-haren ta'addanci da aka kai kan makarantu a kasashen duniya a shekarun baya baya nan ya karu, don haka ya yi kira ga kasashen duniya da su dauki matakai don tabbatar da tsaron makarantun dake yankuna masu fama da rikice-rikice.

Brown ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a cibiyar MDD dake birnin New York a wannan rana cewa, a cikin shekaru biyar da suka wuce, yawan hare-haren da aka kai kan makarantu a sassan duniya ya zarce dubu 10, kuma kananan yara miliyan 28 ba sa iya zuwa makarantu a yankunan da ke fama da rikice-rikice da yanayin dokar ta baci.

Kana Brown ya bayyana cewa, kasashen Nijeriya, Pakistan da sauran kasashe suna hadin gwiwa tare da hukumomin duniya kamar MDD wajen kara azama ga kiran tabbatar da tsaron makarantu, tare da tabbatar da ganin kananan yara sun je makaranta ta hanyar kai dalibai yanki mai tsaro, kafa makarantu masu tsaro, kara daukar matakai a yayin da aka shiga halin dokar ta baci da dai sauransu. Kana Brown ya bukaci da a gudanar da wannan kira a kasashen Lebanon, Sudan ta Kudu, Congo Kinshasa da sauran kasashen duniya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China