in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministocin harkokin wajen Amurka da Iran sun yi shawarwari a kan batun nukiliyar Iran
2015-03-16 20:50:16 cri

A yau ne, sakataren harkokin wajen kasar Amurka John Kerry da ministan harkokin wajen kasar Iran Javad Zarif suka yi shawarwari a birnin Lausanne na kasar Switzerland, inda suka yi kokarin ci gaba da kawar da sabani da zummar cimma wata yarjejeniya kafin karshen wannan wata.

A wani shirin gidan talabijin na CBS na Amurka, mista Kerry ya ce, idan Iran ta tabbatar da cewa, za ta yi amfani da makaman nukiliya ne domin wanzar da zaman lafiya, to, watakila za a cimma wata yarjejeniyar siyasa ta wucin gadi nan da 'yan kwanaki masu zuwa.

Sa'an nan, a jiya Lahadi kafofin yada labaru na Iran sun ruwaito mista Zarif na cewa, idan kasashe 6 da batun nukiliyar Iran ya shafa sun bayyana fatansu na cimma yarjejeniya a siyasance kamar yadda Iran take yi, to, za a cimma wata yarjejeniya. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China