in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Isra'ila ya ki amincewa da yarjejeniya kan batun nukiliyar Iran da mai yiwuwa za a cimma
2015-03-04 14:53:38 cri
A jiya Talata firaministan kasar Isra'ila Benjamin Netanyahu, ya bayyana rashin amincewar sa da yarjejeniyar da mai yiwuwa ne a amince da ita game da batun nukiliyar kasar Iran. A cewar sa yarjejeniyar za ta taimakawa Iran din mallakar makaman nukiliya, da kuma sanya aka yi takarar makaman nukiliya a yankin ta.

Netanyahu ya bayyana hakan ne a gaban 'yan majalisar dokokin kasar Amurka, yana mai cewa yarjejeniyar da ake shirin amincewa sam bata da dace ba.

Ya ce yarjejeniyar ta amince da kasar Iran da ta kiyaye na'urorin samar da makamashin nukiliya, ta yadda za ta iya samun isassun kayayyakin da take bukata don kera makaman nukiliya cikin gajeren lokaci, don haka a ganin sa yarjejeniyar rahusa ce ga kasar Iran.

Bayan jawabin na firaminista Netanyahu, shugaba Barack Obama na Amurka ya bayyana cewa, Netanyahu bai gabatar da shirin da zai iya maye gurbin yarjejeniyar batun nukiliyar kasar Iran, da watakila za a amince da ita ba.

A wani ci gaban kuma, game da jawabin Netanyahu, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Iran Marziyeh Afkham, ta ce jawabin Netanyahu wani wasan kwaikwayo ne na aringizon kalamai, wanda ke kunshe da sakon masu tsattsauran ra'ayi dake Tel Aviv, gabanin zaben shugaban kasar dake tafe. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China