in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka ta sanar da sassauta takunkumin da ta kakaba wa Iran
2014-01-21 13:56:27 cri
Kasar Amurka ta sanar da sassauta takunkumin da ta kakaba wa kasar Iran a ran 20 ga wata, bayan da kasar Iran ta fara aiwatar da yarjejeniyar taron Geneva da aka cimma kan batun nukiliyar kasar a matakin farko.

Kakakin majalisar gudanarwa ta kasar Amurka Jen Psaki ta ba da wata sanarwa, inda ta nuna cewa, sakataren harkokin wajen kasar John Kerry ya riga ya amince da wasu matakan sassauta takunkumin da kasarsa ta kakaba wa kasar Iran, kuma zai sanar da majalisar dokokin kasar game da batun a wannan rana. Sa'an nan kuma, majalisar gudanarwa ta gabatar da cikkaken bayani kan yadda za ta sassauta takunkumin, da suka hada da amincewa da kamfanonin shida na kasar cigaba da sayan man fetur daga kasar Iran, bude wa Iran hanyar biyan kudaden harkokin jin kai, jinya, karatun daliban kasar dake ketare, zama mambar MDD.

Ban da wannan kuma, cikin watanni shida da kasar Iran zata gudanar da yarjejeniyar, Amurka za ta soke takunkumin kan kasar dangane da fitar da kayayyakin man fetur, karafa masu daraja da kuma takunkumin da ya shafi masana'antun motoci.

A ran 20 ga wata, hukumar makamashin nukiliyar kasa da kasa ta tabbatar da cewa, kasar Iran ta fara aiwatar da yarjejeniyar da aka kulla yayin taron Geneva a mataki na farko, matakin ya hada da dakatar da aikin tace sinadarin uranium mai inganci, da kuma surka sinadarin uranium mai inganci da ta riga ta samu da sauransu.

A ran 24 ga watan Nuwamba na shakarar da ta gabata, kasar Iran da kasashen shida da batun nukiliyar kasar ya shafa sun cimma yarjejeniya ta makakin farko a yayin taron Geneva, inda kasar Iran ta yarda da dakatar da wasu ayyukanta game da nukiliya, muddin kasashem yammaci suka sassauta takunkumin da suka kakaba mata, sa'an nan kuma, a ran 12 ga watan da muke ciki, bangarorin da abin ya shafa sun cimma ra'ayi daya kan matakan da za a dauka don aiwatar da yarjejeniyar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China