in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan za a kammala karshen shawarwarin batun nukiliyar Iran cikin yanayi mai kyau
2015-02-16 09:56:53 cri
Jiya Lahadi 15 ga wata, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi wanda a halin yanzu ke ziyarar aiki a kasar Iran ya gana da takwaransa na kasar Mohammad Javad Zarif, kana bayan ganawar tasu, Wang Yi ya bayyana cewa, ya kamata bangarorin shida da batun nikiliyar kasar Iran ya shafa su dukufa tare da kasar Iran domin kawo karshen shawarwarin batun nukiliyar kasar Iran cikin yanayi mai kyau.

Wang Yi ya kuma jaddada cewa, cikin shawarwarin da ake yi dangane da batun, kasar Sin tana tsayawa tsayin daka kan neman hanyar zaman lafiya wajen warware matsalolin da abin ya shafa da kuma nuna adalci, inda ta ba da gudumawa yadda ya kamata cikin harkokin shiga tsakani. Haka kuma, kasar Sin tana son ci gaba da yin hadin gwiwa da bangarorin da batun nukiliyar kasar Iran ya shafa, ta yadda za a iya ci gaba da ba da gudumawa wajen warware batun nukiliyar kasar Iran cikin yanayi mai kyau. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China