in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a kafa cibiyar al'adun Sin a Senegal
2015-01-02 16:07:28 cri
Bisa wata yarjejeniyar da jakadan kasar Sin dake kasar Senegal Xia Huang da ministan al'adu da watsa labarai na kasar Senegal Mbagnic Ndiaye suka kulla, an ce, za a kafa cibiyar al'adun kasar Sin a babban birnin kasar Senegal, Dakar.

Jakadan kasar Sin Xia Huang ya bayyana cewa, za a kafa cibiyar ce domin kiyaye al'adu daban daban daga bacewa.

A jawabinsa Mbagnic Ndiaye ya yi imani cewa, kafuwar cibiyar al'adun kasar Sin za ta kara taimakawa al'ummomin kasar sanin al'adun kasar Sin, tare da ciyar da harkokin al'adun kasar Senegal gaba.

Ya zuwa yanzu, kasar Sin ta kafa cibiyoyin al'adu guda biyar a wasu kasashen Afirka da suka hada da Mauritius, Benin, Tanzania, Nijeriya da kuma Masar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China