in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta taya Hage Geingob murnar zama shugaban Namibia
2014-12-03 20:31:11 cri
Yayin taron manema labaran da aka saba yi a yau Laraba 3 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana cewa, kasar Sin ta taya kasar Namibia murnar gudanar da babban zaben shugaban kasar lami lafiya da kuma jam'iyyar SWAPO da Hage Geingob murnar lashe babban zaben.

Ta ce, tun da dadewa, jama'ar kasashen Sin da Namibia suna goyon bayan juna da fahimtar juna, sun kuma samu sakamako mai gamsarwa kan fannoni daban daban bisa hadin gwiwa da shawarwarin dake tsakaninsu. Gwamnatin kasar Sin ta mai da hankali sosai kan bunkasuwar dangantakar kasashen biyu, wannan ya sa take son ci gaba da inganta dangantakar hadin gwiwa a tsakanin kasashen biyu zuwa wani sabon matsayi, ta yadda zai tallafawa jama'ar kasashen biyu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China