in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban majalisar bada shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin ya gana da tsohon shugaban kasar Namibia
2013-11-23 17:09:44 cri
Yau Asabar 23 ga wata a nan birnin Beijing, shugaban majalisar bada shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin Yu Zhengsheng ya gana da tsohon shugaban kasar Namibia Samuel Dineal Nujoma, inda Yu Zhengsheng ya yaba wa kokarin tsohon shugaban wajen inganta hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Namibia a shekaru da dama da suka gabata. Yu Zhengsheng ya ce, ana samun ci gaba a dangantakar diplomasiyya dake tsakanin Sin da Namibia cikin shekaru 23 da suka gabata. Ya ce, Sin tana fatan ci gaba da kokari tare da kasar Namibia wajen fadada hadin gwiwa a fannoni daban daban don amfanar jama'ar kasashen biyu.

Kana Yu Zhengsheng ya bayyana cewa, inganta hadin gwiwar dake tsakanin Sin da kasashen Afirka muhimmin tushe ne na manufofin harkokin wajen kasar Sin. Har ila yau Sin tana burin kara yin mu'amala tare da bangarori daban daban, da kara yin hadin gwiwa a tsakaninta da kasashen Afirka, da kuma sa kaimi ga samun zaman lafiya da bunkasuwa a nahiyar Afirka.

A nasa bangare, Nujoma godiya ya yi ga kasar Sin domin gudummawar da take bayarwa wajen sa kaimi ga samun bunkasuwa a Afirka. Kana ya bayyana cewa, kasarsa ta dora muhimmanci kan raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin, kuma tana son kara yin hadin gwiwa a fannonin siyasa, da tattalin arziki, da cinikayya, da al'adu da dai sauransu. Bugu da kari, kasarsa tana burin koyon fasahohin Sin a fannin bunkasa tattalin arziki da kyautata zaman rayuwar jama'a, da kuma kara sada zumunta a tsakaninta da kasar Sin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China