in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Nijeriya ya kai ziyara a Namibia
2014-03-21 20:36:12 cri
A Jiya Alhamis 20 ga wata shugaban kasar Nijeriya, Goodluck Jonathan ya isa Windhoek, babban birnin kasar Namibiya inda ya fara ziyarar aiki na tsawon kwanaki biyu.

A yayin da yake tattaunawa da takwaransa na Namibia, Hifikepunye Pohamba, Goodluck Jonathan ya bayyana cewa, gwamnatin Nijeriya za ta dora muhimmanci kan batun yaki da ta'addanci, kuma ta riga ta yanke shawarar kara daukar matakai masu karfi, domin yaki da kungiyar Boko Haram dake arewa maso gabashin kasar Nijeriya. A don haka Shugaba Jonathan yayi fatan gwamnatin Namibia za ta ba da goyon baya da taimako a wannan fanni

Bayan haka, a yayin da wata ganawa da yayi da 'yan Nijeriya mazauna Namibia, shugaba Jonathan ya ce, ko da yake yanzu Nijeriya na fuskantar matsalar cin hanci da rashawa,duk da haka ana zuzuta wannan batu abin da ke yin babbar illa ga mutuncin jama'a da kasar Nijeriya.

.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China