Wata jaridar kasar ta labarta cewa, jirgin na hanyar sa ne ta zuwa birnin Windhoek, hedkwatar kasar. Ya kuma yi hadarin ne jim kadan da tashin sa.
Tuni dai ministan tsaron kasar ta Namibia Nahas Gideon Angula, ya mika sakon ta'aziya ga iyalai, da 'yan uwan wadanda hadarin ya ritsa da su. A hannu guda kuma an fara gudanar da bincike kan musabbabin aukuwar hadarin. (Fatima)