Manzon musamman na shugaban kasar Sin kuma ministan gidaje da raya birane da garuruwa na kasar Sin Chen Zhenggao ya halarci bikin jana'izar marigayi shugaban kasar Zambiya Michael Chilufya Sata tare da ganawa da mukadashin shugaban kasar Guy Scott.
A madadin shugaba Xi Jinping, da gwamnatin Sin da jama'arta, Mr. Chen ya isar da sakon ta'aziyyar shugaba Xi game da rasuwar marigayi Michael Sata tare da mika sakon jaje ga Guy Scott da kuma iyalan marigayi shugaba Sata.
A jawabinsa Guy Scott ya bukaci Mr Chen da ya mika godiyarsa ga shugaba Xi da jama'ar kasar Sin. Ya ce, halartar jana'izar da manzon musamman na Sin ya yi ya nuna irin sahihin zumunci dake tsakanin jama'ar kasashen biyu. Kasar Zambiya kuma za ta ci gaba da bin manufar da shugaba Sata ya kan dauka wato kara zurfafa hadin kai da sada zumunci da kasar Sin nan gaba. (Amina)